Shaikh Zakzaky ya fara da taya jaje ga mahalartan zaman juyayin, wadanda suka fito daga sassa daban-daban na kasar nan. Yace: “Zan fara da taya mu jajen musibar da ta auka ma gidan Manzon Rahma (S). Bayan rashin Manzon Allah din, da kuma duk abubuwan da aka yi, sannan karshe ya karata da shahadar Sayyidatu Nisa’il Alamin (SA), wanda ya auku, za mu iya cewa a rana mai kamar ta yau.”
Ya bayyana Shahadar Sayyida Zahra (S) da abubuwan da suka faru kafin Shahadarta a matsayin “Musiba babba da ta shafi al’umma gabadaya, musamman ma magoya bayan iyalan gidan Annabi (S).” Yace: “Domin su suka san da musibar, su kuma suka san irin abinda ya samu al’umma sakamakon wannan abin, a yayin da mafi yawan ‘yan al’ummar ba su san da wannan ba. Ba kawai basu san da shi ba, akwai ma wadanda suke musanta aukuwarsa.”
Jagora ya yi bitan falala da darajar Sayyida Zahra (S) wanda Manzon Allah (S) yace, “Ita ce shugaban matan Aljanna.” Yace, don haka ta fi duk matan talikai daraja. “Ka ga ace, al’umma gabadaya ta jahilceta, bata santa ba, wannan ba karamin musiba ba ne.”
Jagora ya bayyana dalilin yin jajen Shahadar Sayyida Zahra (S) a lokuta daban-daban, musamman a tsakiyar watan Jimadal Ula da kuma a uku ga watan Jimadat Thani, inda yace, hakan saboda ruwayar da aka samu ne wanda aka kasa bambance kwanaki 75 ne, ko 95 ake nufi tsakanin wafatinta da na Babanta (S), saboda yanayin rubutun zamanin da, wanda bashi da dige-dige.
Shaikh Zakzaky ya bayyana yadda wadanda suka zalunci Sayyida Zahra (S) suka bayyana manufarsu na yin wannan aikin a sarari ba tare da boyewa ba, shi ne kare muradin mulkinsu. Inda ya nuna mamakinsa ga wanda suke kokarin basu uzuri akan abubuwan da suka yi wanda yake kamar hasken rana.
Jagora ya yi bitan ta’annutin da aka yi ga Sayyida Zahra (SA) bayan wafatin Babanta (S), inda aka kai hari, aka cinna wuta a kofar gidanta, aka caka mata karfen da ke tokare kofa, ya karya kashin awazanta, har ta yi barin cikin da take da ita, tare da marinta, da kama mijinta da sunan kai shi ya yi bai’a ga Khalifa. Inda Jagora ya bayyana cewa, abu ne tabbatacce da idan mutum ya bincika zai gani, kar a ce Shi’a ne suka rubuta.
Ya kuma ba da amsa ga masu cewa, ya za a ce an mata haka a gaban Ali, alhali shi jarumi ne? A nan ne ya yi bitan irin wasiyoyin da Manzon Rahma (S) ya yi ga Amirulmuminin Ali (AS), inda ya bashi labarin abubuwan da za su faru da shi a bayansa, har ta kai ma ga Amirulmuminin kan fadi abut un kafin ya faru, saboda wannan masaniyar, da kuma yi masa wasiyya akan yin hakuri. Yace: “Manzon Allah ya umurce shi, yace mashi ya daure, ya bashi labarin duk abinda zai faru sanka-sanka.”
Ya kara da cewa, “Duk abinda ya farun nan gabadaya an gaya masa, kuma an ce ya daure. Daurewan da ya yi ne kuwa ya sa suka iya (masa hujumin). Shi yasa suke cewa, ai shi an masa wasiyya, kuma ba zai kauce ma wasiyyar Annabi ba, ko me muka yi masa ba zai rama ba.”
Jagora ya kuma karanto yadda aka yi mata janaza, aka bizne ta da daddare,bisa wasiyarta ga Amirulmuminin (AS) akan kada ya yarda wadanda suka zalunce ta su yi mata sallah. Yace: “Don haka Imam Ali tare da mutum shida, su bakwai suka yi mata sallah. Har ma a ruwaya ya zo cewa, su wadannan da suka tsaya tare da Ali aka yi sallah din nan daga sahabbansa, albarkacinsu ake yin ruwan sama. Har ma in ana wuyan ruwa, in aka yi tawassuli da su, to yanzu sama za ta yi ruwa.”
Ya jaddada jaje akan yadda ya zama an boye kabarin Sayyida Zahra (SA) saboda tsoron cutar da ita, tunda akwai wadanda suka yi yunkurin a nuna musu su hako su mata sallah, wanda a nan ne Amirulmuminin ya zare musu takobi. Yace: “Ba wanda ya san inda kabarinta yake, har izuwa yanzu din nan. Sai dai in danta Imam (AJ) ya zo, zai nuna inda aka bizne mahaifiyarsa. Amma har yanzu a boye yake.”
Da yake ba da amsa ga masu ganin cewa, tarihin wani abu ne da ya wuce, ko babu bukatar tunawa da shi. Shaikh Zakzaky yace: “Ku baku san irin musibar da ya dubi al’ummar nan sakamakon wannan ba? Sakamakon wannan ne wannan al’umma ta fada cikin musibar da ta fada har yanzu.”
Ya kara da cewa: “In kuma kace mana, ai tarihi ne, a bar shi ya wuce. Sai mu ce maka in haka nan ne kuma, ai komai ma, har addinin ma gabadaya sai a tattara a bar shi, don tarihi ne. Kuma tunda addinin ta wajensu ya gangaro mana, to lallai abinda ya faru a tsakaninsu, dole ya shafi addinin.”
Yace: “Na shan fadan cewa, muna tsakanin tsoro biyu; tsoron boye gaskiya, da tsoron fitinar mutane. Za ka boye gaskiya ne? Ko kuwa za ka fadi gaskiyan ne mutane su fitinu?” Yace: “sai ka yi baina-baina. Baka yi boye gaskiya ba, baka kuma fitini mutane ba. Wanda ke bukatar shiriya, in yana son ya shiriya, kamata ya yi ya bi ta hanya a hankali har ya fahimta, ba nan da nan da ya ji abu ya yi fada da abin ba.”
Ya kuma yi nasiha ga mabiya tafarkin Ahlulbaiti (AS) akan bin wasiccin Amirulmuminin (AS) na yin magana da mutane daidai da hankalinsu. Inda yace: “Wasu suna ganin kamar burgewa ne su fadi maganar gatsar. Kuma su kansu in ma sun shiriya, inda wannan gatsal din aka musu, da basu shiriyan ba. Saboda haka dole ka yi magana da mutane da tausayi. Ba burgewa ne ka fadi magana gatsal ba.”
Yace: “Ana kokari a shiryatar da mutane ne, ba a batar da su ba. In ya zama yadda baka iya magana ba, ka yi maganar da ya zamana sanadiyar wani maimakon ya shiriya ya bace, kana da laifi, domin Manzon Rahma (S) da kyakkyawan usulubi ya isar da sako ga mutane, har yana magana da mutane marhala-marhala ne, yana magana da mutane da daidai gwargwadon darajojin fahimtarsu.”
Don haka ya bukaci a sanya lura da dabara wajen sanar da al’umma Mazlumiyar Ahlulbait (AS) maimakon yi masu baro-baro. Yace: “Ka san wani lokaci in kana gaya ma mutum magana, in ka gaya masa gatsal, ba ganewa zai yi ba, gara ka ahhala shi, shi ya gano da kansa, sai ya fi fahimta.”
Ya kuma yi nasiha akan al’umma da su guji musanta abinda suke ji na zaluntar Ahlulbaiti (AS) da aka yi, inda ya yi kira ga wadanda suke da damar bincikawa kan su bincika ne su gano gaskiya, don su yi riko da sahihin addini. “Wasu da zaran an ce musu ga abinda ya faru, ina! Ai sai fada da zage-zage. Kaga sun dode kofar su fahimci komai.”
A karshe, Jagora ya jaddada godiyarsa ga Allah Ta’ala da tagomashin da ya mana na fahimtar hakikanin sahihin addini, da ilimin da Manzon Rahma (S) ya bari, wanda duk da an yi kokarin rufe shi don kokarin tabbatar da mulkin wasu mutane, amma Allah Ya nufa a sani.
Da yake bayani dangane da darussan da ake dauka daga tunawa da Masa'ib din Ahlulbaiti (AS), Jagora ya bayyana cewa: “Darussan da ke tare a cikin tuna Musibobin Ahlulbaiti (AS) yana da yawa. Na farko, kun ga muna raya al'amarinsu. Kun ga muna kara son su. Kun ga muna koyon dauriya daga gare su. Kuma muna koyon turjiya, mu cije akan abinda suka ba da rayukansu akai.”
Ya kara da cewa: “Za ka ganmu ƙyam-ƙyam-ƙyam! Har wasu suna cewa za su kwaikwayo mu. Ina ku ina kwaikwayonmu? Wane ku nan! Mu kama hanyar Ahlulbaiti (AS), ka zo ka yi irin namu? Ƙarya kake, ba zai yiwu ba! Kai da Musibar wane ne za ka tuna ka dake?” Ya tambaya.
Yace: “Wanda suke bin Ahlulbaiti (AS) su ne za su iya dakewa. Amma kuma kun san a cikin mabiya din, ba kowane ne mabiyi ba fa. Don Imam Jafarus Sadiq (AS) ya yi gaskiya da yace, 'akwai masoyanmu, akwai masu ci da sunanmu.' To masu ci da sunan Ahlulbaiti su ma in suka danna a guje, sai sun fi sauran 'yan Ƙungiya ma zubawa a guje, saboda su suna son su ci da sunan Ahlulbaiti ne. Allah Ya sa mu cikin masoya, ba maciya da sunan Ahlulbaiti (AS) ba.”
A karshe, Jagora (H) ya yi addu'a akan Allah Ta'ala Ya yi maganin masu wa al'ummar kasar nan barazanar za su zo su yi kashe-kashe da sunan baiwa Kiristoci kariya. Yace: "Allah Ta'ala Ka yi mana maganin Trumpopi da na can, da na gida, don a nan ma muna da Trumpopi. Allah Ka yi mana maganinsu.
Allah Ta'ala muna rokonka, duk mai neman al'ummar Musulmi da sharri, Allah ka maida masa sharrinsa. Allah Ka daukaka Musulunci ka kaskanta Kafirci. Ka sa mu cikin jumlar wadanda za ka yi amfani da su wajen dawo da addinin nan. Ka bamu dauriya ka sa mu dake, har izuwa samun nasara, ko kuma mu cika kafin nasara. Ka gaggauta bayyanar wanda da bayyanarsa ne za a samu mafita. Ka saka mu cikin dakarunsa, in mun mutu kafin lokacin ka dawo da mu. Bi hakki Muhammadin wa alihid Dahirin.”
Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)
14/Jimada Ula/1447
05/11/2025
Your Comment